Home / Labarai / An Nada Matar Gwamnan Bauchi Sarauniyar Bauchi

An Nada Matar Gwamnan Bauchi Sarauniyar Bauchi

Imrana Abdullahi
Mai Martaba Sarkin Bauchi Alhaji Dokta Rilwanu Suleiman Adamu, ya ba wa Uwargidan Gwamna Bala Mohammed Sarautar Sarauniyar Bauchi.
Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wani sakon da Ajiyan Bauchi da Babban Limamin Bauchi suka idda sako daga fadar Mai Martaba.
A wannan hoton za a iya ganin Gwamnan Jihar Bauchi tare da Matarsa lokacin da aka kawo sakon sarautar da aka ba matar Gwamnan.
Saboda wannan karamci shugaban ma’aikatan fadar Gwamnatin Jihar Bauchi ya fitar da sanarwa ta shafinsa na facebook, yana cewa “Muna godiya. Allah ya kara wa Sarki daraja. Amin

About andiya

Check Also

Nenadi  Usman Ce Shugabar Jam’iyyar Lebo A Najeriya – Kotun Daukaka Kara

Kotun Daukaka Kara ta shiyyar Owerri ta tabbatar da cewa shugabancin Jam’iyyar Labour Party na …

Leave a Reply

Your email address will not be published.