Daga Imrana Abdullahi
A kokarin ganin an kara karfafa dankon zumunci a tsakanin al’ummar tarayyar Najeriya da kuma jama’ar wadansu kasashe kungiyar Zabi Sonka ta kasa reshen Jihar Kaduna sun kaddamar da kalandar da ke dauke da hotunan ya’yan kungiyar, sarakuna da kuma shugabannin al’umma daban daban.

Alhaji Danjuma Furana tare tare da dimbin ya’yan kungiyar sun bayyana gamsuwa da irin kwazo tare da hadin kan da ya’yan kungiyar suka bayar wajen ciyar da kungiyar da kasa gaba.
Da yake tofa albarkacin bakinsa Alhaji Sallau Dan mato Tokarawa daga jihar Kano ya bayyana irin wannan kokarin na samar da Kalandar kungiya a matsayin wani babban al’amarin da kowa zai yi alfahari da shi.

An dai yi taron ne a harabar gidan rediyon Quen FM da ke garin Zariya, taron dai ya samu halartar dimbin ya’yan kungiyar daga ciki da wajen Jihar Kaduna
THESHIELD Garkuwa