Home / Labarai / AN GA WATAN AZUMI A NAJERIYA – SARKIN MUSULMI

AN GA WATAN AZUMI A NAJERIYA – SARKIN MUSULMI

MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI
Bayanan da muke samu daga fadar Mai alfarma Sarkin musulmi Alhaji Sa’adu Abubakar III, ya tabbatar da ganin watan Ramadana mai alfarma a Najeriya.
Wanda hakan ya tabbatar da cewa a gobe ne daya ga watan Ramadana don haka a gobe za a tashi da Azumi kenan.
Mai alfarma Sarkin musulmi ya bayyana Jihohin Kano, Borno, Sakkwato da sauran wadansu Jihohin ma da dama da aka ga watan Azumin.
Alhamdulillah! Mai alfarma Sarkin Musulmi ya baiyana ganin jinjiri watan Ramadan na wannan shekara 1443.AH.
Gobe ta kasance daya ga watan Azumi.
Allah Ya bamu ikon gabatar da ibada a cikin nasara.

About andiya

Check Also

Nenadi  Usman Ce Shugabar Jam’iyyar Lebo A Najeriya – Kotun Daukaka Kara

Kotun Daukaka Kara ta shiyyar Owerri ta tabbatar da cewa shugabancin Jam’iyyar Labour Party na …

Leave a Reply

Your email address will not be published.