Home / Labarai / Allah Ya Yi Wa Shugaban Kungiyar Ma’aikatan Kananan Hukumomi Ta Kasa Rasuwa

Allah Ya Yi Wa Shugaban Kungiyar Ma’aikatan Kananan Hukumomi Ta Kasa Rasuwa

Allah Ya Yi Wa Shugaban Kungiyar Ma’aikatan Kananan Hukumomi Ta Kasa Rasuwa

Mustapha Imrana Abdullahi
Kwamared Abdullahi Muhammad Gwarzo shugaban kungiyar Ma’aikatan Kananan hukumomi ta kasa reshen Jihar Kano ya sanar da rasuwar shugaban kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi ta kasa Kwamared Ibrahim Khaleel.
Marigayin ya rasu ne a babban asibitin Abuja kuma kafin rasuwarsa shi ne ma’ajin kungiyar kwadago ta kasa 
Kamar yadda sanarwar ta bayyana cewa za a yi Jana’izar mamacin a garin Wudil karamar hukumar Wudil da ke cikin Jihar Kano da Yammacin yau Alhamis idan Allah ya kaimu. 
Allah ya gafarta masa ya albarkaci abin da ya bari.

About andiya

Check Also

Nenadi  Usman Ce Shugabar Jam’iyyar Lebo A Najeriya – Kotun Daukaka Kara

Kotun Daukaka Kara ta shiyyar Owerri ta tabbatar da cewa shugabancin Jam’iyyar Labour Party na …

Leave a Reply

Your email address will not be published.