Home / Labarai / MTN Ya Dauke A Unguwannin Rigachikun Da Mando

MTN Ya Dauke A Unguwannin Rigachikun Da Mando

Mustapha Imrana Abdullahi
Bayanan da wakilin mu ya tattara na bayanin cewa layin wayar hannu na MTN ya dauke a unguwannin Mando da Rigachikun da ke karamar hukumar Igabi a cikin Jihar Kaduna.
Bayanan da muka tattara daga wajen jama’ar wannan yankin sun bayyanawa wakilin mu cewa lamarin baya rasa nasaba da kokarin da ake yi na dakile ayyukan yan Ta’adda musamman a wannan lokacin da ake fafutukar yaki da su.
Wanda hakan ya sa a Jihohin Katsina da Sakkwato aka dakile layukan wayar sadarwa a wasu kananan hukumomi, sai kuma a Jihar Zamfara nan ma wayar hannun ba ta aiki.

About andiya

Check Also

Nenadi  Usman Ce Shugabar Jam’iyyar Lebo A Najeriya – Kotun Daukaka Kara

Kotun Daukaka Kara ta shiyyar Owerri ta tabbatar da cewa shugabancin Jam’iyyar Labour Party na …

Leave a Reply

Your email address will not be published.