Home / Labarai / Muna Bukatar Yan Sandan  SARS  A Jihar Zamfara – Matawalle

Muna Bukatar Yan Sandan  SARS  A Jihar Zamfara – Matawalle

Muna Bukatar Yan Sandan  SARS  A Jihar Zamfara – Matawalle

Mustapha Imrana Andullahi
Gwamnan Jihar Zamfara Alhaji Dokta Muhammad Bello Matawallen Maradun ya bayyana cewa su a Jihar Zamfara suna bukatar jami’an tsaron yan sandan SARS saboda irin aikin da suke gudanarwa a Jihar.
Gwamna Matawalle ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa da manema labarai jim kadan bayan ya fito daga taron kungiyar Gwamnonin Arewacin Nijeriya da aka yi a Kaduna.
Matawalle ya ce su matsayinsu a Jihar Zamfara Shi ne suna bukatar jami’an tsaron yan Sandan SARS sakamakon irin kwazon aikinsu, don haka ya kara da cewa suna bukatar a zakulo su a duk inda suke a kawo masu su a Jihar Zamfara suna bukatarsu.

About andiya

Check Also

Nenadi  Usman Ce Shugabar Jam’iyyar Lebo A Najeriya – Kotun Daukaka Kara

Kotun Daukaka Kara ta shiyyar Owerri ta tabbatar da cewa shugabancin Jam’iyyar Labour Party na …

Leave a Reply

Your email address will not be published.