Home / Labarai / Sanata Abdul’Aziz Yari Ya Kara Tallafawa Jama’a Da Abinci Da Karatun Yara A Jihar Zamfara

Sanata Abdul’Aziz Yari Ya Kara Tallafawa Jama’a Da Abinci Da Karatun Yara A Jihar Zamfara

Daga Imrana Abdullahi

Bayanan da muke samu daga Jihar Zamfara na cewa Sanata Abdul’Aziz Yari Abubakar ya kaddamar da rabon kayan abinci ga magidantan Talatar Mafara da ke cikin Jihar Zamfara.

Bayanan da muka samu ya tabbatar mana cewa kowane magidanta guda biyu an ba su kwali daya su raba da katon kwallin ya kunshi Taliya, Makaroni da Shinkafa”.

Bayan haka kuma ya dauki nauyin dalibai kowace karamar hukuma a fadin kananan hukumomi 14 na Jihar da za a zakulo mashi a kalla dalibai dari da Hamsin da zai dauki nauyin tallafin karatunsu a makarantun jami’a ko kwalejojin ilimi, kwalejin kimiyya da fasaha da kuma kwalejin horon malamai.

Wanda a halin yanzu dai ana ganin fagen siyasar Jihar Zamfara ya fara daukar sabon salo musamman ma na tafiya da daukacin al’umma baki daya.

About andiya

Check Also

Nenadi  Usman Ce Shugabar Jam’iyyar Lebo A Najeriya – Kotun Daukaka Kara

Kotun Daukaka Kara ta shiyyar Owerri ta tabbatar da cewa shugabancin Jam’iyyar Labour Party na …

Leave a Reply

Your email address will not be published.