Daga Imrana Abdullahi Gwamnan jihar Zamfara, Muhammad Bello Matawalle, ya bayyana a fili a wajen wani babban taron Shekara shekara na kungiyar marubuta a kafofin yada labarai mai su na ( Arewa Media Writers) da aka yi a garin Kaduna cewa shugabannin arewa ke da alhakin matsalar tsaron da ya …
Read More »Yan Bindiga Sun Sace Sarki Kpop Ham Mai Daraja Ta Daya
Mustapha Imrana Abdullahi Rahotannin da muke samun a halin yanzu daga Jihar Kaduna na cewa yan bindiga sun sace wani Sarki mai daraja ta daya Kpop Ham, Dokta Jonathan Danladi Gyet Maude (JP, OON) wanda sanannen Sarki ne kuma jagoran al’ummar Jaba cikin Jihar Kaduna. Rahotannin da muke samu na …
Read More »Gwamna Matawalle Zai Gabatar Da Jawabi A Wajen Taron Matasa A Kan Harkar Tsaro
 Imrana Abdullahi Gwamnan Jihar Zamfara Bello Muhammad Mutawalle zai gabatar da kasida a game da kalubalen tsaro, ci gaban Siyasa yadda lamarin ya shafi arewacin Nijeriya. Zai gabatar da jawabin ne a babban taron marubuta a kafafen yada labarai na arewacin Najeriya da za a yi a ranar Lahadi …
Read More »GWAMNA BALA MUHAMMAD YA MARABCI, MASARAUTA A GIDAN GWAMNATI
Gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Abdulkadir Muhammed ya marabci majalisar Masarautar Bauchi da ta kai masa gaisuwar sallah karkashin jagorancin me martaba Sarkin Bauchi Dakta Rilwanu Suleiman Adamu. Da yake jawabi, Gwamna Bala ya alakanta nasarorin da gwamnatin sa ke samu da goyon baya da hadin kai da masu …
Read More »A Daina Fadin Abin Da Ba Shi Ake Aikatawa Ba – Makarfi
Mustapha Imrana Abdullahi Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Ahmad Muhammad Makarfi, ya yi kira ga daukacin al’umma baki daya da su daina fadin abin da ba shi suke aikatawa ba. Sanata Ahmad Muhammad Makarfi ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganawa da manema labarai a Kaduna jim kadan bayan …
Read More »Masarautar Jama’a ta soke bukukuwan Sallah
Mai Martaba Sarkin Jama’a dake kudancin jihar Kaduna, Alhaji Muhammad Isa Muhammad II ya bi sauran manyan masarautu dake jihohin da aka bayyana tsoron alamun bayyanar cutar korona wajen dakatar da bukukuwan Sallar layya. Sarkin, yayi wannan kira ne a yau cikin takardar manema labarai da …
Read More »Sallar Idi: A Yi Wa Buhari Da El- Rufa’i Addu’ar Samun Nasarar Kalubalen Tsaro – Sardaunan Badarawa
Daga Wakilin Mu YAYIN da al’ummar Musulman duniya ke sake gudanar da wani bikin babbar Sallar Layya (Idi-El-Kabir) don tunawa da sadaukarwa da biyayya ga umarnin Allah da Annabi Ibraham da dansa Ismail, tsohon shugaban rikon karamar hukumar Kaduna ta Arewa Honarabul Usman Ibrahim, wanda aka fi sani da Sardaunan …
Read More »Kotu Ta Iza Keyar Abduljabbar Zuwa Gidan Yari
Mustapha Imrana Abdullahi Kotu a Jihar Kano ta caji Shaikh Abduljabbar Nasiru Kabara, da laifin yin batanci, tunzura jama’a sakamakon hakan ta mika ajiyarsa gidan gyaran hali, wato kurkukun da ke Kano. Indai Za’a iya tunawa Shaikh Abduljabbar Nasiru Kabara, Malamin addinin musulunci ne da ke Kano wanda ya rika …
Read More »Gwamnan Jihar Zamfara Ya Bada Umarnin A Biya Albashi Da Kudin Alawus Alawus
Mustapha Imrana Abdullahi Gwamnan Jihar Zamfara Muhammad Bello Matawalle ya bayar da umarnin a biya daukacin ma’aikatan Jihar kudin albashinsu da kuma kudin alawus alawus domin al’ummar Jihar su samu sukunin yin bukukuwan Sallah cikin walwala da annashuwa. Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata takardar sanarwar da ke …
Read More »NUJ Ta Karrama Muhammad Rabi’u Musa
Mustapha Imrana Abdullahi Sakamakon irin kokarin taimakawa rayuwar al’umma ba tare da nuna bambanci ko gajiyawa ba ya sa kungiyar yan jaridu ta kasa (NUJ) reshen kamfanin wallafa jaridun New Nigeria da Gaskiya Ta Fi Kwabo suka ga dacewar Karrama Alhaji Muhammad Rabi’u Musa da lambar girmamawa domin kara masa …
Read More »
THESHIELD Garkuwa